2019-11-30 15:52:33 cri |
Taron da aka kaddamar a ranar 25 ga watan da muke ciki, na da nufin baiwa bangarorin kasar Syria damar kara musayar ra'ayi kan wasu batutuwan, da suka hada da gyara tsarin mulkin kasar. Dukkan bangarorin 2 na kasar Syria sun gabatar da ta su ajandar shawarwari, tare da musayar su don ci gaba da tantance su. Duk da haka, sun kasa cimma ra'ayi daya kan wasu batutuwan da suka hada da mulkin kai, da aikin yaki da ta'addanci, da sakin fursunoni, da dai sauransu. Lamarin da ya hana gudanar da taron daukacin mambobin kungiyoyi daban daban karkashin kwamitin tsarkake mulkin kasar Syria.
Geir Pedersen ya kara da cewa, ya yi kokarin lallashin shugabannin kwamitin da suka wakilci bangarori 2 na kasar Syria, don neman su cimma daidaito, amma hakarsa ba ta cimma ruwa ba. (Bello Wang)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China