Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
MDD ta bukaci a gaggauta daukar matakin kare annobar farin dango a yankin kahon Afrika
2020-02-11 09:46:30        cri
MDD ta bukaci al'ummomin kasa da kasa su gaggauta daukar matakan da za su taimaka wajen kare annobar farin dango a kahon Afrika, yayin da lokaci ke kurewa kasashen yankin, a kokarin su na shawo kan kutsen kwarin.

Mataimakin sakatare janar na MDD kan ayyukan jin kai, Mark Lowcock, ya shaidawa manema labarai jiya a hedkwatar majalisar dake birnin New York cewa, barazanar farin a yankin kahon Afrika babban kalubale ne.

Ya ce akwai mutane miliyan 30 a kasashen da batun ya shafa, da suka hada da Habasha da Kenya da Somalia, wadanda kuma ke cikin tsananin rashin wadatar abinci. Yana mai cewa a yanzu, mutane miliyan 10 na wuraren da farin suka shiga.

Mark Lowcock, ya ce idan har ba a dauki mataki cikin makonni 3 zuwa 4 masu zuwa ba, za a fuskanci matsala mai tsananin gaske. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China