Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Jami'in MDD zai halarci taron kolin AU mai take kawar da karar bindiga
2020-02-06 11:42:54        cri
Babban sakataren MDD Antonio Guterres zai halarci taron kolin kungiyar tarayyar Afrika (AU) karo na 33, wanda aka shirya gudanarwa tsakani 9 zuwa 10 ga watan Fabrairu, a hedkwatar kungiyar mai mambobin kasashen Afrika 55 dake Addis Ababa, na kasar Habasha.

A cikin wata sanarwar da MDD ta fitar a ranar Laraba ta bayyana cewa, ana sa ran Guterres zai gabatar da jawabi a taron kolin na AU. Taken taron kolin wannan shekarar shi ne "Kawar da karar bindiga, samar da ingantaccen yanayin cigaban nahiyar Afrika."

Babban sakataen MDD zai yi wata ganawa da mambobin kasashen, kana zai halarci wasu taruka, daga bisani zai gabatar da jawabi a taron manema labarai a ranar 8 ga watan Fabrairu.

A lokacin da jami'in MDDr ya isa Habasha zai halarci wasu taruka don kammala cimma matsaya kan wasu batutuwan hadin gwiwa da AU, da suka hada da shirya babban taro game da batun daidaiton jinsi da bunkasa cigaban matan Afrika da kaddamar da shirin asusun shugabancin matan Afrika, a ranar 8 ga watan Fabrairu.

Sauran batutuwan kuma, sun hada da batun samar da damammakin raya cigaban tattalin arzikin Afrika ta hanyar albarkatun teku, wanda ya kunshi shirin hadin gwiwar nahiyar, wanda ake sa ran gudanarwa a matsayin wani muhimmin bangare a taron kolin na AU.(Ahmad Fagam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China