Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Babban jami'in MDD ya bukaci a gaggauta tsakaita bude wuta a arewa maso yammacin Syria
2020-02-02 19:43:52        cri
Sakatare janar na MDD Antonio Guterres a ranar Asabar ya bukaci a gaggauta tsakaita bude wuta tsakanin bangarorin dake yaki da juna a arewa maso yammacin Syria.

A sanarwar da kakakinsa ya fitar, babban sakataren MDD ya nuna damuwa matuka game da ayyukan da sojoji ke gudanarwa a shiyyar.

Babban sakataren ya ce hare-haren da ake kaiwa kan fararen hula da kuma kan wasu muhimman kayayyakin more rayuwar jama'a, kamar asibitoci, ba abin da za'a lamunta ba ne.

Sanarwar ta ce, duk wani nau'in aikin sojoji daga kowane bangare, wanda ya hada da daukar matakai kan kungiyoyin ta'addanci da wanda kungiyoyin ke kaddamarwa, dole ne su mutunta muhimman dokokin jin kan bil adama na kasa da kasa, wanda ya kunshi baiwa fararen hula cikakkiyar kariya.

Guterres ya nanata cewa babu wani matakin soji da zai iya warware matsalolin tashin hankali. (Ahmad Fagam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China