2020-01-13 10:57:15 cri |
A shekarar 2019 da ta gabata, kasar Sin ta ci gaba da dukufa kan aikin yaki da cin hanci da karbar rashawa. Kuma bisa kididdigar da kafofin watsa labaran kasar suka yi, an ce, daga watan Janairu zuwa watan Oktoba, gaba daya an kama wadanda suka aikata laifin cin hanci da karbar rashawa suka gudu zuwa kasashen waje guda 1634, kudaden da aka kwato sun kai RMB miliyan 2954, adadin da ya karu matuka idan aka kwatanta da na shekarar 2018.
A shekarar 2020 kuma, kasar Sin za ta ci gaba da kyautata tsarin sa ido na Jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin da na gwamnatin kasar Sin, domin karfafa aikin bincike da sa ido kan masu rike da mukamai (Maryam)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China