Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Bai kamata sauran kasashe su yanke hukunci kan batun hakkin dan Adam na Sin ba, in ji kakakin Kambodiya
2019-12-13 10:33:37        cri
Da yammacin jiya Alhamis ne kakakin kasar Kambodiya Phay Siphan, ya bayyana cewa, batun yaki da ta'addanci a yankin Xinjiang, batu ne na cikin gidan kasar Sin, kuma dokar hakkin dan Adam kan jihar Xinjiang da majalisar wakilan Amurka ta zartas ba ta da ma'ana ko kadan, bai kamata sauran kasashe su yanke hukunci kan batun hakkin dan Adam na wata kasa ta daban ba.

Haka kuma, ya ce, ba kawai batun jihar Xinjiang yana shafar zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar Sin ba ne, har ma yana da muhimmanci ga zaman lafiya da zaman karko na yankin baki daya. Ya ce, gwamnatin kasar Sin ta dauki matakan yaki da ta'addanci a jihar Xinjiang, domin kiyaye zaman karko da zaman lafiyar kasar kanta, tana kuma ba da gudummawa wajen kiyeye zaman lafiyar yankin baki daya.

Dokar hakkin dan Adam kan jihar Xinjiang ta kasar Sin da majalisar wakilan kasar Amurka ta zartas, ta zama lamarin tsoma baki cikin harkokin gidan kasar Sin, ta kuma bata sunan kasar Sin, a wani yunkuri na hura wutar rikici a kasar. Kazalika an samar da wannan doka ne bisa dalilai na siyasa, ba bisa dalili na doka ba, wanda hakan ya kasance wata hujja ta kasar Amurka, wadda ta kan yi amfani da ita wajen tsoma baki cikin harkokin gidan sauran kasashe. (Maryam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China