![]() |
|
2019-12-04 14:36:26 cri |
Rahotanni na cewa, manufar kafa da kuma gudanar da cibiyar koyar da sana'o'i a Xinjiang ita ce kawar da tushen yaduwar ta'addanci da tsattsauran ra'ayin addini, matakin da ya cimma nasarar hana aukuwar ayyukan ta'addanci da kare rayuwa da dukiyoyin jama'ar kabilu daban-daban a wurin.
Kasar Sin tana kalubalantar Amurka da ta yi watsi da bambancin ra'ayi a siyasance kan kasar Sin, da kuma jingine matakan da ta dauka na matsawa kasar Sin lamba, kana ta dakatar da zargin kasar Sin ba bisa gaskiya ba, da daina tsoma baki a harkokin cikin gidan kasar Sin, da dakatar da yin abubuwan da za su bata hadin kan kasashen biyu kan aikin yaki da ta'addanci. (Amina Xu)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China