Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Sin ta mai da martani kan dokar hakkin Bil Adama na Uygur da Amurka ta gabatar
2019-12-04 11:08:16        cri

Yau Laraba, mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen Sin, madam Hua Chunying ta yi tsokaci kan dokar hakkin Bil Adama na kabilar Uygur ta jihar Xinjiang da Amurka ta gabatar, inda ta ce, dokar ta illata yanayin hakkin Bil Adama a jihar Xinjiang, har ta shafa bakin fenti kan ayykan da Sin take yi na kawar da tsattsauran ra'ayi da ta'addanci, da kuma takalar manufar da gwamnatin Sin ke dauka wajen gudanar da harkokin jihar, matakin da ya keta dokar kasa da kasa da ka'idar dangantakar kasa da kasa, kuma shisshigi ne cikin harkokin cikin gidan kasar Sin, wanda Sin ba ta ji dadinsa ba, kuma ba za ta yarda da shi ba.

Jihar Xinjiang ta kasar Sin na fama da masu tsattsauran ra'ayi da ayyukan ta'addanci. Saboda ganin irin hali mai tsanani da take ciki, gwamnatin jihar ta dauki matakan da suka dace don dakile su, a sa'i daya kuma, tana mai da hankali kan kawar da asalin wadannan mummunan ayyuka, ciki hadda sa kaimi ga aikin kawar da tsattsauran ra'ayi, matakin da ya ba da tabbacin cewa, ba a samu ayyukan ta'addanci a jihar ba har tsawon shekaru 3 a jere, hakan ya sa mutanen jihar miliyan 25 ke farin ciki sosai da maraba da wadannan manufofi, matakin da ya taka rawa ga aikin yaki da ta'addanci a duniya.

Ban da wannan kuma, kasashen duniya na yabawa wadannan manufofi sosai. Saboda haka, matakin da Amurka ta dauka ya sabawa hakikanin halin da ake ciki da ra'ayin al'ummar duniya, Hua ta yi gargadin cewa, harkokin jihar Xinjiang harkokin cikin gidan kasar Sin ne, ba wanda zai iya tsoma baki a ciki. Kuma ta yi kira ga Amurka da ta daina yin kuskure, tare da dakatar da zartas da wannan doka da tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasar Sin, tana mai cewa, Sin za ta mayar da martani ga duk matakin da Amurka za ta dauka. (Amina Xu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China