Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Xi Jinping zai ziyarci Girka da kuma halartar taron shugabannin kasashen BRICS karo na 11
2019-11-07 20:14:05        cri
Daga ranar 10 zuwa ranar 15 ga watan nan, shugaban kasar Sin Xi Jinping, zai yi ziyarar aiki a kasar Girka, sa'an nan, zai isa kasar Brazil, domin halartar taron shugabannin kasashen BRICS karo na 11 da za a yi a birnin Brasilia.

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Qin Gang, ya bayyana a yau Alhamis cewa, ziyarar shugaba Xi a kasar Girka, za ta raya dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen Turai, tare da karfafa hadin gwiwar dake tsakanin bangarorin biyu game da shawarar "Ziri daya da hanya daya".

Kana, halartar shugaba Xi taron ganawar shugabannin kasashen BRICS, zai kasance muhimmin aikin diflomasiyya da kasar Sin za ta yi, da sauran kasashe masu tasowa, da ma kasashe masu saurin samun bunkasuwar tattalin arziki. (Maryam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China