![]() |
|
2019-08-16 15:35:13 cri |
Mohammad Javad Zarif ya bayyana a kan Intanet a wannan rana cewa, Amurka ba za ta cimma burinta ba ta aiwatar da irin wannan mataki, hakan ya sa tana nufin amfani da doka da shari'a yadda take so, don kwace dukiyar Iran a haddin ruwan tekun jama'a, lamarin da ya bayyana cewa, gwamnatin Donald Trump ba ta mutunta shari'a da doka ko kadan.
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Birtaniya ya nuna a wannan rana cewa, Birtaniya ta gano cewa, mahukuntan Gibraltar sun sami takardar shaidu daga bangaren Iran dake bayyana cewa jirgin ruwan ba kasar Sham zai tafi ba. Kakakin na neman Iran ta cika alkawarinta, ya ce, Birtaniya ba za ta amince Iran ko daidaikun mutane su yi jigilar man fetur zuwa Sham ba, domin matakin ya keta takunkumin da EU ta kakkabawa kasar Sham. (Amina Xu)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China