Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Ana fargabar 'yan ci rani 150 sun mutu ko sun bata bayan kwale-kwalensu ya kife a gabar tekun Libya
2019-07-26 10:49:10        cri

Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD UNHCR, ta yi kiyasin 'yan ci rani 150 sun bata, inda ake fargabar sun mutu, biyo bayan kifewar kwale-kwalensu na katako a gabar ruwan Libya.

Kakakin hukumar Charlie Laxley, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, baya ga 'yan ci ranin 150 da ake fargabar sun mutu a jiya Alhamis, masu tsaron gabar tekun Libyan sun ceto wasu mutane 150.

Saboda yanayin rashin tsaro da rikici, biyo bayan hambarar da mulkin marigayin Muammar Gaddafi a shekarar 2011, Libya ta zama hanyar da dubban 'yan ci rani ke bi domin tsallake tekun Bahar Rum zuwa Turai. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China