Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kwamitin sulhu na MDD ya yi Allah wadai da harin da aka kai cibiyar tsare 'yan ci-rani dake kasar Libya
2019-07-06 15:51:54        cri
Kwamitin sulhu na MDD, ya yi Allah wadai da wani harin da aka kai wata cibiyar tsare 'yan ci-rani dake dab da Tripoli, hedkwatar kasar Libya a kwanakin baya, lamarin da ya yi sanadiyyar asarar rayukan mutane 53, gami da raunata wasu fiye da 130.

Cikin wata sanarwar da ya fitar a jiya, kwamitin sulhun ya jaddada bukatar saukaka yanayin da ake ciki a Libya ga bangarorin dake adawa da juna a kasar, sannan ya bukaci su cika alkawarin da suka yi na tsagaita bude wuta. A cewar kwamitin, ba za a iya samun zaman lafiya da kwanciyar hankali mai dorewa a kasar ta Libya ba, idan har ba a bi hanyar siyasa da shawarwari ba.

Kwamitin sulhun mai kunshe da mambobi 15, ya bayyana damuwa matuka kan tsanantar yanayin jin kai a kasar Libya, inda suka bukaci bangarori masu ruwa da tsaki na kasar, su samar da cikakkun damammakin gudanar da aiki ga hukumomi masu kula da ayyukan jin kai. (Bello Wang)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China