2019-06-26 13:46:14 cri |
Bayan da ya halarci taron tabbatar da sakamakon da aka cimma a taron kolin FOCAC jiya Talata a Beijing, Mohamed Taha Siala ya bayyana cewa, kasarsa wato Libya na goyon-bayan wasu manyan matakai takwas da shugaba Xi Jinping ya bullo da su a wajen taron koli na Beijing na dandalin tattaunawa kan hadin-gwiwar Sin da Afirka wato FOCAC, yana kuma fatan Libya za ta karfafa hadin-gwiwa da Sin a fannonin da suka shafi murkushe ayyukan ta'addanci da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankinsu.
Har wa yau, Mohamed Taha Siala ya ce, Libya na nuna himma da kwazo wajen shiga cikin ayyukan shawarar "ziri daya da hanya daya", inda ya jaddada cewa, kasarsa na son taka rawar gani wajen inganta hadin-gwiwa da mu'amala da kasar Sin a fannoni daban-daban.(Murtala Zhang)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China