Ranar 2 ga watan Oktoba, kasar Gambia da ke yammacin nahiyar Afirka ta sanar da fita daga kungiyar kasashe renon Ingila, lamarin da ya sanya raguwar yawan kasashen dake cikin kungiyar daga 54 zuwa 53. Kasar ta Gambia, wadda kasar Ingila ta taba yiwa mulkin mallaka, ta shiga kungiyar ta Commonwealth ne a shekarar 1965.