in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta mai da martani game da yanke huldar diplomasiyya da Gambiya ta yi da Taiwan
2013-11-15 20:30:12 cri
A ranar Jumma'ar nan 15 ga wata, ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta mai da martani game da labarin da wasu kafofin yada labarai suka bayar na cewar, kasar Gambiya ta ce, ta yanke huldar diplomasiyya da yankin Taiwan, inda ta ce, sanin cewar kasar Sin guda daya ce a duniya abu ne da kasashen duniya suka tabbatar.

A ranar Alhamis ne dai Gambiya ta sanar da cewa, ta yanke huldar diplomasiyya da yankin Taiwan bayan shekaru 18, kamar yadda wasu kafofin yada labarai suka ruwaito.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin Hong Lei ya ce, ma'aikatar ta samu wannan labarin ne ta wasu kafofin yada labarai na kasashen waje domin Gambiya ba ta tuntubi kasar Sin ba game da hakan.

Mr. Hong ya ce, kasar Sin guda daya ce tak a duniya, amincewa da hakan da bin yadda yake abu ne da duk kasashen duniya suka sani, kuma ba da goyon baya ga kasar don ganin ta ci gaba da samun dawwamammen zaman lafiya da hadin kai, abu ne da ake bukata a ko da yaushe.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China