in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Gambia ta fita daga kungiyar kasashen renon Ingila
2013-10-03 16:37:27 cri
Kasar Gambia da ke yammacin nahiyar Afirka ta bayyana sanarwar ficewa daga kungiyar kasashe renon Ingila.

Wata sanarwar da kasar ta fitar a maraicen ranar Laraba 2 ga watan Oktoba ta ce, gwamnatin kasar ta Gambia ta janye daga cikin kungiyar ta Commonwealth, kana ta yanke shawarar cewa, ba za ta sake shiga kungiyar da ke da nasaba da wani na'u'i na mulkin mallaka ba.

Wannan matakin da kasar ta dauka ya zo ne kimanin shekaru 50 bayan da kasar ta Gambia ta shiga kungiyar ta Commonwealth a shekara 1965, ko da ya ke sanarwar ba ta yi wani karin bayani ba. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China