in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta fitar da jadawalin hajojin da za ta dagewa karin haraji
2019-05-14 09:51:50 cri
Nan ba da jimawa ba ne kasar Sin za ta tattara, tare da fitar da cikakken jadawalin hajojin Amurka da ake shigarwa kasar wadanda ba za ta karawa haraji ba, bayan da ta gudanar da bincike da tantance dalilan hakan.

Hukumar kwastam mai buga haraji karkashin majalissar zartaswar kasar ce ta bayyana hakan, tana mai cewa, wadanda suka gabatar da bukatar dage musu karin harajin, za su iya cimma nasarar samun hakan ne kawai, idan sun gabatar da gamsassun dalilai, na ko dai rashin madadin irin wadannan hajoji, ko matsanancin yanayi na tattalin arziki da za su iya fuskanta, ko mummunan tasiri da sashen masana'antun su zai fuskanta, ko tasiri maras kyau ga zamantakewar al'umma.

Bisa aniyar Amurka ta karawa hajojin Sin da darajar su ta kai dala biliyan 200 harajin kaso 25 bisa dari daga kaso 10 bisa dari, tun daga ranar 10 ga watan Mayun bana, a jiya Litinin ita ma Sin ta sanar da aniyar kara harajin ta ga hajojin Amurkar da ake shigarwa Sin, tun daga ranar 1 ga watan Yuni mai zuwa.

Gabanin hakan Sin ta kara haraji kan wasu hajojin Amurka da darajar su ta kai dala biliyan 60, kana za ta sake kara wa irin wadannan hajoji harajin kaso 25 da kaso 20 da kuma kaso 10 bisa dari. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China