Kasar Sin na neman kara albashi ga ma'aikata
Rahotanni daga kasar Sin na cewa, akwai ma'aikata kimanin miliyan 200 da aiki a kasar, wadanda kusan kashi 80% daga cikinsu na kula da ayyuka dake da alaka da samar da kayayyaki, gami da aikin gini. Tun bayan da gwamnatin tsakiya ta kasar Sin ta gabatar da wasu manufofi na kyautata kwarewar ma'aikata, gami da karin albashi, bangarorin da lamarin ya shafa a kasar, suka kaddamar da matakai daban daban a kwanakin baya. Bayanai na cewa, ya zuwa yanzu an gabatar da matakan karin albashin ma'aikata, da ba su damar sayen hannayen jari a kamfanonin da suke aiki, da ba su tallafin sayen gida, da makamantansu, a larduna fiye da 20 na kasar ta Sin. (Bello Wang)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku