in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masanin Burtaniya kan harkokin kasar Sin: Ya zama dole kasashen yammaci su gano wata hanyar cudanya da kasar Sin
2019-05-07 21:47:35 cri
Masanin kasar Burtaniya kan harkokin kasar Sin, wanda kuma shi ne babban manazarci a jami’ar Cambridge, Mr. Martin Jacques a kwanan baya ya rubuta cewa, dole ne kasashen yammacin duniya, musamman ma Amurka su gano wata hanyar cudanya da kasar Sin, a maimakon su ci gaba da nuna girman kai. Ya ce kamata ya yi Amurka ta saba da sabon yanayin da duniya ke ciki, kuma ta mutunta kasar Sin a matsayin abokiyar takararta, ta yadda za ta gano wata sabuwar hanyar yin hadin gwiwa da kasar Sin da kuma fuskantarta. A sharhinsa mai taken “What China Will Be Like as a Great Power”, Martin Jacques ya ce, “Babbar matsalar da kasashen yamma suke fuskanta ita ce rashin fahimtar kasar Sin da zurfin tunaninmu, wato a ganinmu, kasashen yamma na iya wakiltar kowa, kuma salon zamani daya a duniya, wato irin salon zamani na kasashen yamma.” Sai dai ra’ayin bai iya zaunawa da gindinsa ba, sabo da ba kawai sauye-sauye na faruwa a kasar Sin ba, kasashe masu tasowa da dama ne suka bambanta da kasashen yamma ta fannonin tarihi da siyasa da kuma al’adu. A cikin irin wannan hali ne, ya zama dole kasashen yamma su yi kokarin fahimtar bambancin da ke tsakaninsu da kasar ta Sin. (Lubabatu)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China