in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin ya gana da takwaransa na Habasha
2019-04-25 10:02:12 cri

Firaministan kasar Sin Li Keqiang, ya gana da takwaransa na Habasha, Abiy Ahmed, a jiya Laraba, gabanin taro na 2 na hadin gwiwar kasa da kasa karkashin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, wanda zai gudana daga yau Alhamis zuwa Asabar 27 ga wata, a nan birnin Beijing.

Da yake bayyana muhimmancin dangantakar dake tsakanin Sin da Afrika, Li Keqiang ya ce a shirye kasar Sin take ta yi aiki da Habasha wajen zurfafa hadin gwiwarsu karkashin Ziri Daya da Hanya Daya da kuma aiwatar da sakamakon da aka cimma yayin taron koli na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afrika da aka yi a bara.

Ya ce kasar Sin ta shirya zurfafa hadin gwiwa da Habasha a fannonin samar da ababen more rayuwa da mara baya ga raya yankunan da layin dogon da ya tashi daga Addis Ababa zuwa Djibouti ya ratsa, yana mai cewa za a karfafawa kamfanonin kasar Sin gwiwar zuba jari a Habasha.

A nasa bangaren, Firaminista Abiy Ahmed, ya ce Habasha na daukar Sin a matsayin muhimmiyar abokiyar hulda, kuma a shirye take ta inganta hadin gwiwarta da Sin a fannoni daban daban, domin zama abun misali ga kungiyar kasashe masu tasowa da kuma hadin gwiwar Sin da Afrika. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China