Kafin hakan, kudurin dokar ya samu amincewa a zauren majalissar wakilan kasar gabanin babban zaben kasar na watan Fabarairu.
Da yake tabbatar da hakan, babban mataimakin shugaban kasar game da harkokin majalissar dokoki Ita Enang, ya ce za a fara aiwatar da sabon tsarin albashin ne nan take.
A cikin watan Nuwambar bara ne dai kungiyar kwadago ta Najeriya ta shiga wani yajin aiki na sai baba ta gani, domin matsawa gwamnati lamba, sakamakon zargin da ta yi cewa, gwamnatin ka gaza wajen cika alkawarin da ta dauka na tabbatar da karin albashi. (Saminu Alhassan)