in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Watakila gobara ta fara tashi ne daga karkashin hasummiyar majami'ar Notre Dame
2019-04-18 11:29:32 cri

Jami'in kula da binciken gobarar da ta tashi a majami'ar Notre Dame na kasar Faransa Remy Heitz, ya bayyana a ranar 17 ga wata cewa, mai yiwuwa ne tsautsayi ya haddasa tashewar gobarar. Bisa binciken da aka yi a mataki na farko, an ce, watakila gobara ta fara tashi ne daga karkashin hasummiyar majami'ar.

Mr Heitz ya bayyana cewa, bisa binciken da aka yi a halin yanzu, tsautsayi ne ya haddasa tashin gobara. Abin mai wuya ne a yi binciken, idan aka gama aikin gyara ginin majami'ar, za a kara sauri wajen yin binciken.

An ce, 'yan sanda 40 da jami'an hukumomin shari'a fiye da 10 sun fara yin binciken, wadanda suka bada tambayoyi ga mutanen da suke gyara majami'ar kafin tashin gobarar. Bisa labarin da mutane masu kallon batun suka bayar, watakila gobarar ta fara tashi ne daga karkashin hasummiyar majami'ar dake dab da gabar kogin Seine.

Gobara ta tashi a majami'ar Notre Dame a ranar 15 ga wannan wata, inda ta lalata rufin dakin da hasummiyar majami'ar, amma an kiyaye babban ginin majami'ar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China