in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Macron ya yi alkawarin sake gina majami'ar Notre Dame cikin shekaru 5
2019-04-17 10:31:38 cri
Shugaban kasar Faransa Emanuel Macron, ya yi alkawarin sake gina babbar majami'ar nan ta Notre Dame wadda gobara ta lakume cikin shekaru 5 masu zuwa. Shugaba Macron ya yi wannan alkawari ne a jiya Talata, yana mai kira ga al'ummar kasar Faransa da su hade kan su wuri guda.

Cikin wani gajeren sakon talabijin da ya gabatar ga al'ummar kasar, shugaban Macron ya ce "Za mu sake gina Notre Dame, ta yadda majami'ar za ta fi da kayatarwa, ina kuma son ganin an kammala aikin cikin shekaru 5 ".

Da yammacin ranar Litinin ne dai gobara ta lakume ginin majami'ar. Wasu hotunan da aka yada ta kafafen yanar gizo sun nuna yadda hayaki ya turnuke rufin hasumiyar majami'ar, yayin da wuta ke cin sassan ginin dake tsakanin manyan kararawa biyu dake saman ta.

Duk dai da cewa ba a fayyace kiyasin adadin asarar da aka yi sakamakon gobarar ba, amma tuni sassa daban daban suka yi alkawarin taimakawa da kusan kudi har Euro miliyan 700, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 790, domin sake ginin majami'ar mai tarihin shekaru kusan 850.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China