Labarin ya tsamo sanarwar da bangaren soja na kasar Chadi ya bayar a ranar 15 ga wata cewa, dakarun sun kai hari da daddare. Sojojin kasar Chadi 7 sun mutu a sakamakon aikin soja da aka yi na martani ga harin, kana sojoji fiye da 10 sun ji rauni.
Wannan ne karo na biyu da aka yi musayar wuta mai tsanani a tsakanin sojojin kasar Chadi da kungiyar Boko Haram a cikin wata guda. Bisa labarin da kafofin watsa labaru suka bayar, sabon hafsan hafsoshin sojojin kasar Chadi Tahir Erda ya bayyana a yayin da yake yin rangadin aiki a sansanin yaki da ta'addanci a kwanakin baya cewa, ana bukatar daukar sabbin matakai don yaki da kungiyar Boko Haram. (Zainab)