Majalissar kolin Sudan ta sha alwashin hukunta wadanda suka hallaka masu zanga zanga
Majalissar kolin soji dake mulkin wucin gadi a kasar Sudan, ta sha alwashin hukunta wadanda suka hallaka masu zanga zanga a kasar. Shugaban kwamitin siyasa na majalissar Omer Zainal-Abdin ne ya bayyana hakan, biyowa bayan hambarar da gwamnatin Omar al-Bashir a jiya Alhamis.
Zainal-Abdin ya kuma bayyana aniyar majalissar, game da yiwuwar rage wa'adin aikin majalissar daga shekaru biyu zuwa kasa da hakan. Kaza lika Mr. Zainal-Abdin ya ce ba za a mika tsohon shugaban kasar Omar al-Bashir ga kotun kasa da kasa ta hukunta manyan laifuka ko ICC ba. (Saminu Hassan)