in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masu zanga-zanga a Sudan na ci gaba da bore domin nuna rashin amincewa da tsarin rundunar sojin kasar
2019-04-12 15:35:51 cri
Wasu daga cikin masu zanga-zanga na kasar Sudan, sun ki amincewa da matakan da rundunar sojin kasar ta sanar, inda suka yanke shawarar ci gaba da zaman dirshan a gaban hedkwatar rundunar sojin.

Kungiyar kwararru dake adawa da gwamnatin kasar, ta yi watsi da sanarwar da ministan tsaron kasar Awad Mohamed Ahmed Ibn Auf ya yi.

Kungiyar ta jaddada cikin wata sanarwa cewa, za ta ci gaba da zaman dirshan har sai lokacin da aka mika mulki ga gwamnatin farar hula.

Ita ma kungiyar fafutukar 'yanci da sauyi ta The Freedom and Change Alliance, ta yi watsi da sanarwar da rundunar sojin ta fitar, ta na mai kira ga magoya bayanta da su ci gaba da zaman dirshan.

Haka zakalika ita ma Jam'iyyar adawa ta Sudanese Congress, ta yi biris da sanarwar ta rundunar sojin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China