in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bangarori daban daban na Afirka sun yaba wasikar murnar kafa cibiyar nazarin Afirka ta Sin da shugaba Xi Jinping ya aike
2019-04-10 11:23:06 cri
A jiya ne, aka gudanar da taron kafa cibiyar nazarin Afirka ta Sin a nan birnin Beijing, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aike da wasikar murnar kafa cibiyar. Bangarorin al'umma daban daban na kasashen Afirka sun bayyana cewa, shugaba Xi Jinping ya dora muhimmanci sosai ga hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka, kuma za a yi amfani da kwararrun masana kan harkokin Sin da Afirka dake cibiyar wajen kara samar da gudummawa kan raya dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka.

Farfesa Sheriff Ibrahim masanin harkokin siyasa da dangantakar kasa da kasa na Jami'ar Abuja dake Nijeriya ya bayyana cewa, kafa cibiyar muhimmin mataki ne da zai taimaka wajen cimma muradun Sin da Afirka, lamarin da ya shaida cewa, Sin tana son kara fahimta da yin mu'amala a tsakaninta da kasashen Afirka.

Shugaban kungiyar hadin gwiwa da raya kasa kan hadin gwiwar dake tsakanin Afirka da Sin ta kasar Morocco Nasser Busheba ya bayyana cewa, akwai bukatar yin nazari don kara inganta hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka, ya yi imani cewa, cibiyar za ta taka muhimmiyar rawa wajen kara yin mu'amalar al'adu da ilmi a tsakanin Sin da kasashen Afirka, matakin da zai taimaka wajen inganta dangantakar dake tsakaninsu.

Babban sakataren watsa labaru na shugaban kasar Uganda Don Vanyama ya bayyana cewa, kwararrun masana kan harkokin Sin da Afirka a cibiyar. Za su taimaka ga zurfafa dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka da sada zumunta a tsakaninsu. A sakamakon hadin gwiwa tare da kasar Sin a fannoni daban daban, kasar Uganda za ta kara samun moriya da fasahohi. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China