in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane a kalla 50 sun mutu a sakamakon musayar wuta da ta faru a kasar Nijeriya
2019-04-06 20:40:27 cri
Hukumar kiyaye tsaro ta farin kaya ta kasar Nijeriya ta tabbatar a yau cewa, kungiyar 'yan banga da wasu tsageru sun yi musayar wuta a jihar Zanfara dake arewa maso yammacin kasar Nijeriya, wadda ta haddasa mutuwar mutane a kalla 50.

Wani jami'in hukumar ya bayyanawa kamfanin dillancin labaru na Xinhua cewa, an yi musayar wuta ne a ranar 2 ga wata, bayan kungiyar 'yan banga ta yankin Kaura Namoda dake jihar Zanfara ta samu labari cewa, akwai wasu tsageru da suka taru a dajin dake dab da yankin. Daga baya kungiyar ta tura wasu membobinta da kuma wasu jama'a zuwa wurin, inda suka yi musayar wuta.

A wannan rana kuma, shugaban majalisar dokokin jihar Zanfara Sanusi Rikiji ya yi kira ga kungiyar 'yan banga da ta taimakawa ga hukumar tsaron ta farin kaya, domin kada a dauki matakan murkushe tsagerun daga bangare daya ba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China