in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin dindindin na Najeriya a MDD ya yi kira ga al'ummun Afirka da su sake waiwayar tushensu
2019-03-26 21:11:04 cri
Wakilin dindindin na tarayyar Najeriya a MDD Tijjani Muhammad-Bande, ya yi kira ga al'ummun nahiyar Afirka a duk inda suke, da su sanya shekarar nan ta 2019, shekarar da za su sake waiwayar tushensu.

Tijjani Muhammad-Bande, ya yi wannan kiran ne a Litinin din nan, albarkacin ranar MDD ta kasa da kasa, ta tunawa da al'ummun da cinikin bayi da kuma safarar bil Adama ta tekun atlantika ya shafa.

A cewar sa, yayin da ake cika shekaru 400 da kawo karshen cinikin bayi ta tekun atlantika, ita ma majalissar shugabannin kasashe mambobin kungiyar hadin kan Afirka ta AU, a zaman ta na watan Fabarairun da ya gabata, ta yi suka game da yadda aka aikata laifuka na muzgunawa, da ayyukan rashin imani, yayin cinikayyar bayi ta tekun atlantika. Kaza lika ta yi tir da yadda aka kafa wani tsarin nuna wariyar launin fata, da kuntatawa, da nuna kyama da tursasawa bil Adama.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China