in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An Yi Tir Da Hare-haren Kin Jini Da Ake Kai Wa 'Yan Nijeriya A Afrika Ta Kudu
2019-03-29 21:05:50 cri
Labarin da muka samu daga jaridar Leadership A Yau ya nuna cewa, kungiyar 'Yan Nijeriya mazauna kasar Afrika ta kudu (NUSA), ta bayyana bacin ranta a kan zargin kai hare-haren ta'addanci da ake kaiwa 'Yan Nijeriya, musamman hare-haren nuna kin jinin baki na kwanan nan da aka kai kan wasu al'ummun kasashen waje a kasar.

Mataimakin Sakataren kungiyar, Collins Mgbo ne ya nuna bacin ran kungiyar, cikin wata wasikar da kungiyar ta aikewa hukumomin kasar a ranar Laraba.

Mgbo ya ce, an jiwa 'yan Nijeriya bakwai rauni, a lokacin hare-haren da ake ci gaba da kaiwa, uku daga cikin su ma a yanzun haka suna kwance ne a Asibiti, domin raunukan na su sun yi tsanani, inda suke barazana ga rayuwarsu.

Ya ce, akwai bukatar sa bakin gwamnatocin kasashen na Afrika ta kudu, da Nijeriya cikin gaggawa, musamman kan yanda rikicin ke kara tabarbarewa.

Har dai zuwa lokacin hada wannan rahoton, ba labarin mutuwar wani dan Nijeriya, duk da cewa an bayar da labarin mutuwar 'yan kasar waje biyu a sakamakon harin," in ji wasikar ta Mgbo.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China