in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da suka mutu sakamakon rugujewar ginin makaranta a Najeriya ya karu zuwa 18
2019-03-15 09:27:09 cri
Rahotanni daga Najeriya na cewa, yawan mutanen da suka mutu sanadiyar rugujewar wani ginin makaranta mai hawa 3 a Legos, cibiyar kasuwancin kasar, ya karu zuwa 18, yayin da aka kara tono gawawwaki a safiyar jiya Alhamis.

Kwamishinan lafiya na jihar Legas, Jide Idris ya shaidawa manema labarai cewa, an tabbatar da mutuwar mutane 18 kana an ceto sama da mutane 60.

Ya ce, koda yake an kawo karshen aikin ceto da ake yi, amma ana iya ganin ma'aikatan lafiya suna kokarin taimakawa wadanda lamarin ya shafa.

A cewar jami'in, zai yi wahala a halin yanzu a bayyana yawan wadanda lamarin ya shafa a hukumance , ganin yadda ake ci gaba da tattara alkaluman wadanda suka mutu da wadanda suka jikkata.

Yanzu haka dai, akwai a kalla manyan asibitoci uku da wani asibitin kula da kananan yara guda a Legas dake jinyar wadanda hadari ya shafa

Mai magana da yawun babban sakataren MDD Stephane Dujarric, ya shaidawa taron manema labarai cewa, Antonio Guterres ya kadu matuka da hadarin rubtawar ginin da ya faru a Najeriya, yana mai cewa, jami'in na MDD zai aikawa gwamnatin Najeriya sakonsa na ta'aziyya dangane da faruwar wannan iftila'i.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China