in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ziyarar firaministan kasar Sin za ta ingiza matsayin alakar Sin da tarayyar Turai
2019-04-04 14:48:54 cri
Ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, ta ce ziyarar da firaministan kasar Sin Li Keqiang zai gudanar a wasu kasashen nahiyar Turai, za ta ingiza matsayin dangantakar Sin da kasashen Turai, tare da samar da sabon zarafi na inganta kawancen sassan biyu.

Wata sanarwa da ma'aikatar ta fitar, ta ce Mr. Li zai gudanar da ziyarar ne tsakanin ranekun 8 zuwa 12 ga watan Afirilun nan, zai kuma ziyarci birnin Brussels domin halartar taron jagororin Sin da Turai na tattauna makomar sannan a karni na 21.

Kaza lika zai kai ziyarar aiki kasar Croatia, tare da ganawa da shugabannin tsakiya da gabashin Turai na CEEC.

Wannan ce dai ziyarar farko da firaminista Li zai gudanar a ketare cikin wannan shekara, tun bayan ziyarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gudanar a kasashen Italiya, da Monaco da kasar Faransa a watan jiya.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China