in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta zartas da wasu daftarin gyararrun dokoki masu nasaba da dokar zuba jari ta baki 'yan kasuwa
2019-04-04 11:11:24 cri

Jiya Laraba firaministan kasar Sin Li Keqiang, ya shugabanci taron majalisar gudanarwar kasar, inda aka zartas da wasu daftarin dokoki domin taimakawa aiwatar da dokar zuba jari ta baki 'yan kasuwa, a kokarin kyautata yanayin kasuwanci. Yayin zaman an tsai da kudurin rage haraji kan kunshin kayayyaki da matafiya ke shigowa da su kasar, da kuma kayan da ake aikowa ta gidan waya, a wani mataki na fadada hada-hadar shigo da kayayyaki da kuma yin sayayya.

A yayin taron, an zartas da wasu daftarin gyararrun dokoki dangane da gudanar da mulki, tambari, gine-gine, siginar lantarki da dai sauransu, an kuma tsai da kudurin gabatar da su ga zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin don ya duba. An ba da shawarar cewa, za a tanadi "ka'idar rashin nuna bambanci" cikin dokar gudanar da mulki, kana kuma za a kara karfin hukunta wadanda suka keta hakkin yin amfani da tambari, tare da kara yawan kudin diyya.

Har ila yau, a yayin taron, an tabbatar da wasu matakan da za a dauka, domin ganin fararen hula sun kara cin gajiya ta fuskar ganin likita da shan magani. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China