in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masar ta kaddamar da shafin Afrika da harshen Sinanci
2019-04-04 10:08:42 cri
Hukumar yada labaran kasar Masar (SIS), wacce ke sanya ido ga kafafen yada labaran kasashe waje da tantance su, ta sanar a ranar Laraba cewa ta kaddamar shafin intanet game da Afrika da harshen Sinanci.

SIS ta fada cikin wata sanarwa cewa, ta kaddamar da shafin na Afrika ne da harshen Sinanci saboda a shekarun baya bayan nan ana samun karin mua'amalar hadin gwiwa tsakanin kasar Sin da kasashen Afrika, sannan ana samun karin jarin da kamfanonin kasar Sin suke zubawa a kasashen Afrika masu yawa a dukkan fannoni.

Sanarwar ta ce shafin da aka kaddamar zai taimaka wajen samar da muhimman bayanai game da kungiyar tarayyar Afrika AU da hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afrika (FOCAC).

Shafin zai kuma samar da bayanai game da kasashen Afrika kuma zai dinga sabunta muhimman labaran Sin da Afrika, da sharhi da kasidu wadanda suka shafi hulda tsakanin bangarorin biyu, inji SIS.

Shafin na SIS a yanzu yana amfani da harsunan Sinanci, Larabci, Turanci, Faransanci, da yaren Sifaniya. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China