in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An samu gobara a tashar jiragen kasa ta kasar Masar domin sakacin matukin jirgin kasan
2019-02-28 14:14:45 cri

Babban mai gabatar da kararraki na kasar Masar Nabil Sadeq ya bayar da sanarwa a jiya Laraba cewa, an gano dalilin da ya sa aka samu gobara a tashar jiragen kasa ta Ramses dake birnin Alkahira na kasar Masar a wannan rana da safe, an ce sakacin matukin jirgin kasan ne ya haifar da gobarar tuni, an riga an kama wannan matuki.

Bisa labarin da kafofin watsa labaru na kasar suka bayar, hadarin ya haddasa mutuwar mutane a kalla 20 tare da raunatar mutane 43, wasu daga cikinsu sun ji rauni mai tsanani.

Bayan abkuwar hadarin, shugaban kasar Masar Abdel Fattah al Sisi ya bayyana cewa, za a yanke hukunci kan wadanda suka haddasa hadarin, kana ya nuna alhini ga mutanen da suka mutu a sakamakon hadarin. Ministan harkokin sufuri na kasar Hesham Arafat ya yi murabus a wannan rana domin wannan lamari, firaministan kasar Mostafa Madbouly ya amince da takardar yin murabus din sa.

Majalisar ministocin kasar ta amince da samar da kudi ga iyalan mutanen da suka mutu da kuma mutanen da suka ji rauni a sakamakon hadarin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China