Monica Mutsvangwa ta bayyana yayin wani taron manema labarai cewa, abun bakin ciki ne yadda adadin mutanen da suka mutu ya kai 268, kuma har yanzu ana tsammanin karuwarsa yayin da ake ci gaba da aikin bincike.
Ministan kananan hukumomi da ayyukan gwamnati da samar da gidaje na kasar, July Moyo, wanda kuma ke jagorantar aikin binciken, ya ce adadin wadanda suka mutun ya hada da gawarwakin da aka samu rahoton an gansu a saman ruwa a makwabiciyar kasar Mozambique da kuma wadanda aka binne a Zimbabwen. Ya ce gwamnati za ta ci gaba da aikin bincike da ceto. (Fa'iza Mustapha)