Gemme Connel, shugabar ofishin kula da ayyukan jin kai na MDD a yankunan kudanci da gabashin Afrika ce ta tabbatar da karuwar adadin.
Yayin da take ganawa da manema labarai ta wayar tarho jiya, a birnin Maputo na kasar Mozambique, Jami'ar ta ce sama da mutane 195 ne suka mutu a kasashe makwabta, da suka hada da 56 a Malawi da 139 a Zimbabwe, kamar yadda rahotanni daga gwamnatocin kasashen suka bayyana. (Fa'iza Mustapha)