in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Algeria ya ce zai yi murabus kafin ranar 28 ga watan Afrilu
2019-04-02 13:40:27 cri

Shugaban kasar Algeria Abdelaziz Bouteflika ya ce zai sauka daga shugabancin kasar gabanin cikar wa'adin mulkinsa a ranar 28 a watan Afrilu, kamfanin dillancin labaran kasar APS ne ya bada rahoton cikin wata sanarwar da aka fitar daga fadar shugaban kasar.

Sanarwar ta ce, shugaba Bouteflika zai yi murabus kafin ranar 28 ga watan Afrilu, wanda ita ce ranar da wa'adin mulkinsa zai kare.

Wata majiya ta bayyana cewa, Bouteflika zai dauki wannan muhimmin mataki ne bisa tsarin dokar kundin tsarin mulkin kasar, domin tabbatar da ganin ma'aikatu da hukumomin gwamnatin kasar suna ci gaba da tafiyar da al'amurransu yadda ya kamata a lokacin da za'a gudanar sauyin shugabanci a kasar wanda zai fara tun daga ranar da shugaban ya yi murabus.

A daren ranar Lahadi, shugaba Bouteflika ya nada sabbin mambobin hukumar zartaswar kasar wanda firaiministan kasar Noureddine Bedoui ke jagoranta. Makasudin kafa sabuwar majalisar ministocin shi ne, domin tabbatar da ganin an tafiyar da sauyin shugabancin kasar cikin kwanciyar hankali. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China