in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar zaben Algeria ta ce martaba lokacin zabe shi ne zai tabbatar da demokaradiyya
2019-01-21 09:45:48 cri
Babbar hukumar shirya zabe mai zaman kanta ta kasar Algeria ta ce mutunta jadawalin ranakun gudanar da zabe shi ne babban abin da zai tabbatar da tsarin mulkin demokaradiyya.

Kiraye-kirayen da hukumar zaben kasar ta yi inda ta bukaci masu kada kuri'u a zaben shugaban kasar dake tafe, wata alama ce dake tabbatar da cewa kasar Algeria tana yunkurin tabbatar da daya daga cikin muhimman matakan kasa da kasa na samar da shugabanci na gari, Abdulwahab Dirbal, babban jami'in hukumar zaben kasar shi ne ya bayyana hakan ta kafar gidan radiyon kasar.

Tun da farko, Ali Ghediri, tsohon daraktan ma'aikatar tsaron kasar ya sanar da cewa, zai tsaya takarar neman shugabancin kasar a zaben shugaban kasar da za'a gudanar ranar 18 ga watan Afrilu.

Ghediri, mai shekaru 64 a duniya, shi ne mutum na farko da ya bayyana aniyarsa ta neman karawa da shugaban kasar mai ci Abdelaziz Bouteflika, dan shekaru 81 a duniya, wanda ya dare shugabancin kasar tun a shekarar 1999.

A bisa dokar kundin tsarin mulkin kasar, wajibi ne 'yan takarar dake neman shugabancin kasar su yi rajista da kotun tsarin mulki ta kasar kafin ranar 4 ga watan Maris.

Rashin tabbas dangane da ko Bouteflika zai sake tsayawa takarar neman shugabancin kasar ya haifar da rudani a fagen siyasar kasar ta Algerian cikin watannin da suka gabata. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China