in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kafa cibiyoyin yaki da cutar kwalara 11 a yankunan Mozambique da guguwar Idai ta shafa
2019-04-02 09:43:24 cri
Ma'aikatan agaji na MDD a yankunan da guguwar Idai ta lalata, na kokarin dakile yaduwar cutar kwalara, inda suka kafa cibiyoyi 11 a kasar Mozambique kadai.

Kakakin majalisar Stephane Dujarric, ya ce daga cikin cibiyoyin 11 da aka kafa, guda 9 na aiki, ciki har da na yankin Beira da guguwar ta fi shafa.

Ya ce a gobe Laraba ne za a fara riga kafin cutar kwalara. Ya ce cikin sa'o'i 24 da suka wuce, an samu rahoton mutane 258 sun kamu da cutar. Kuma akwai hadarin yaduwar cutar, la'akari da mutane 276 da suka kamu da ita a yankunan da iftila'in ya aukawa.

Ya ce majalisar kula da tattalin arziki da zamantakewa ta MDD, za ta gudanar da taron na musammam game da kai dauki kasashen Mozambique da Malawi da Zimbabwe, da iftila'in ya aukawa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China