in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'an ba da tallafin jin kai na Sin sun isa kasar Mozambique bayan aukuwar ibtila'in guguwar Idai
2019-03-25 20:26:30 cri
Jami'an ba da tallafin jin kai na kasar Sin sun isa kasar Mozambique, bayan da ibtila'in guguwar Idai ya daidaita wasu yankunan kasar, kana tasirin ta ya shafi mutane kimanin 794,000.

Gwamnatin kasar ta bayyana cewa, an samu ceto karin mutane a Beira dake lardin Sofala na tsakiyar kasar, wanda ya sanya adadin wadanda aka ceto kaiwa ga mutum 128,941.

Yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a yau, ministan ma'aikatar filaye, muhalli da raya karkarar kasar Celso Correia, ya ce adadin wadanda suka rasa rayukan su sakamakon ibtila'in ya kai mutum 446.

A dai wannan rana ne kuma, jami'an ba da agajin jin kai na kasar Sin su 65 suka isa filin jiragen sama na Beira, tare da kayan aikin jin kai da nauyin su ya kai tan 20, ciki hadda kayan jiyya, da na aikin zakulo wadanda ibtila'in ya rutsa da su, da kuma kayan sadarwa. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China