in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar bada taimako ta Sin ta fara gudanar da ayyuka a Mozambique
2019-03-29 11:13:28 cri
Tawagar bada taimako ta kasar Sin ta fara gudanar da ayyukan bada gudummawa a jihar Sofala dake tsakiyar kasar Mozambique a ranar 27 zuwa 28 ga watan Maris, wadda ke fama da bala'in mahaukaciyar guguwa mai suna "Idai".

A cikin kwanakin biyu, tawagar bada taimako ta kasar Sin ta tura rukunoni uku don samar da gudummawa ga birnin Beira na jihar, da matsugunar masu fama da bala'in, da yankin kogin Buzi. An ce, tawagar ta bada aikin jinya ga masu fama da bala'in fiye da 500 tare da bayar da magunguna iri iri ga masu fama da bala'in fiye da 400.

A yankin kogin Buzi, rukunin tawagar ya yi bincike kan yanayin gabar kogin don sanin yanayin kogin da hanyar tafiyar kogin da yanayin kauyukan dake gabar kogin, ta hakan za a tsara shirin bada taimako na nan gaba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China