in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mozambique za ta samar da kayayyakin jin kai ga wadanda guguwar Idai ta shafa
2019-03-29 11:26:16 cri
Shugaban kasar Mozambique, Filipe Nyusi, ya ce bayan shafe kwanaki 15 ana aikin bincike da ceton wadanda mahaukaciyar guguwar Idai ta rutsa da su, aikin agajin gaggawa a kasar ya shiga wani muhimmin mataki, inda za a kai kayayyakin agaji ga iyalan da iftila'in ya rutsa da su.

Filipe Nyusi ya bayyana haka ne jiya da yamma a Beira na lardin Sofala, bayan ya tattauna da kungiyoyin agaji daban-daban, da kuma yin shiru na wani lokaci domin girmama wadanda iftil'ain ya shafa.

Ya ce agajin zai kasance karkashin bangarori 5 da suka hada da; tallafin abinci da magunguna da matsuguni da ruwa da kuma tsaftar muhalli.

A cewar shugaban kasar, dawowar harkokin rayuwa a yankunan da iftila'in ya shafa na bukatar sake fasalin agajin da ake bukata, wanda zai mayar da hankali kan ayyukan gona da kayayyakin gini da sauransu.

Shugaba Nyusi ya ce, gwamnati za ta raba kayayyakin aikin gona a yankunan, yana mai alkawarin gaggauta sake gina su domin rayuwa ta koma kamar yadda take a baya.

Ya kuma sanar da matakan magance tasirin rayuwa kan iyalan da iftila'in ya shafa, ta hanyar rage kudin da ake biya a cibiyoyin kiwon lafiya da sufuri da makamashi. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China