in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude taron ingancin ruwa da kare filaye na MDD a Masar
2019-04-01 10:16:29 cri
A jiya Lahadi ne aka bude taron MDD, game da nazari kan matakan inganta ruwa da kare filayen noma daga gurbata. Taron na bana dai na gudana ne a birnin Alkahiran Masar, karkashin jagorancin hukumar samar da abinci da bunkasa ayyukan gona ta MDD ko FAO a takaice.

Taron na yini 5, ya samu halartar kimanin mutane 400, da suka kunshi kwararru, da jami'an gwamnati, da masu tsara manufofi, da sauran sassan masu ruwa da tsaki, musamman daga yankunan gabashi da arewacin nahiyar Afirka da ma sauran yankuna.

Ana dai sa ran mahalarta taron za su yi musayar ra'ayoyi, game da hanyoyin magance karancin ruwa da abinci, da batun inganta dabarun kare filaye daga kwararar hamada, da lalacewar kasa sakamakon fari da sauyin yanayi. Kaza lika za a tattauna game da sauran al'amura masu nasaba da kyautata rayuwar daukacin bil Adama.

Da yake tsokaci game da hakan, mataimakin darakta, kuma wakilin yankunan gabashi da arewacin Afirka a taron Abdessalam Ould Ahmed ya jaddada cewa, za a tattauna bukatun gaggawa na yankunan a 'yan kwanaki masu zuwa, musamman duba da yadda suke da tasiri wajen dakile ci gaban tattalin arziki, da yada talauci. Za kuma a tattauna game da batun karancin guraben ayyukan yi, da batun masu ci rani, lamurran da har kullum, ke yin tarnaki ga zaman lafiya da daidaito a yankunan. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China