in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bukaci Mali ta dauki matakan kare aukuwar munanan hare-hare
2019-03-27 10:27:28 cri
Hukumar kare hakkin dan Adam ta MDD, ta bukaci gwamnatin Mali ta dauki matakan da suka dace na kare aukuwar ayyukan take hakkokin bil adama, bayan wani hari da ya yi sanadin mutuwar mutane a kalla 153 tare da raunata wasu 73 a yankin Mopti.

A cewar kakakin shugaban hukumar Ravina Shamdasani, mummunan harin da aka kai ranar Asabar, ya kara yawan kashe-kashen da ake yi a yankin Mopti, wanda ya samo asali daga rikici tsakanin al'ummomi, da kuma wasu kungiyoyin masu ikirarin kare kansu, dake kokarin fatattakar kungiyoyin masu tsattsauran ra'ayi.

Yayin wani taron manema labarai, Ravina Shamdasani ta ce harin da aka kai Ogossagou na yankin Mopti dake tsakiyar Mali, shi ne na baya-bayan nan cikin jerin hare-hare da rikice-rikice dake faruwa a yankin.

Ta ce daga watan Maris na 2018 zuwa yanzu, wadannan rikice-rikice sun yi sanadin mutuwar mutane 600 da suka hada da mata da maza da yara, yayin da wasu dubbai suka rasa matsugunansu, a yankin Mopti kadai. ((Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China