in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya aika da sakon taya murna ga taron majalisar zartaswar shugabannin AL karo na 30
2019-03-31 16:49:18 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aika da sako zuwa ga takwaransa na kasar Tunisiya Beji Caid Essebsi, wanda kuma shine shugaban majalisar zartaswar shugabannin kungiyar kawancen kasashen Larabawa na wannan zagaye, inda ya taya murnar kaddamar da taron majalisar karo na 30 a birnin Tunis.

Shugaba Xi ya jaddada cewa, kawancen kasashen Larabawa ya dukufa ka'in da na'in wajen shimfida zaman lafiya da kwanciyar hankali da neman ci gaba a yankin Gabas ta Tsakiya, da bada shawarar daidaita matsaloli ta hanyar siyasa, tare kuma da yin kokarin hada kan kasashen Larabawa, wannan babban abun yabawa ne. A watan Yulin bara, an yi taron ministoci karo na 8 na dandalin tattaunawa kan hadin-gwiwar Sin da kasashen Larabawa a birnin Beijing, inda bangarorin biyu suka amince da kafa wata huldar abota bisa manyan tsare-tsar tare da yin hadin-gwiwa da neman ci gaba kafada da kafada, al'amarin da ya kasance sabon mafari na hadin-gwiwar Sin da kasashen Larabawa. Xi ya kara da cewa, Sin tana fatan yin kokari tare da kasashen Larabawa don kara samun fahimtar juna, da inganta hadin-gwiwa da mu'amalar al'adu, da tabbatar da aiwatar da shawarar "ziri daya da hanya daya", don kara kyautata dangantakar abota bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da kasashen Larabawa, tare kuma da bada gudummawa ga raya kyakkyawar makomar bil'adama ta bai daya.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China