in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar bada agajin jiyya ta Sin ta 21 ta koma gida bayan da ta kammala aikinta a kasar Mozambique
2019-01-20 16:37:06 cri
A ranar 19 ga wata, tawagar bada agajin kiwon lafiya ta kasar Sin ta 21 ta koma gida daga birnin Maputo ta jirgin sama bayan da ta kammala aikinta na tsawon shekaru biyu a kasar Mozambique.

Shugaban tawagar Chen Liping ya bayyana cewa, sharadin bada agajin kiwon lafiya na kasar Mozambique yana da koma baya, kuma akwai karancin kayayyakin aikin likitanci sosai, don haka 'yan tawagar sun hada kai sosai tare da likitocin wurin wajen sabunta tunaninsu wajen aikin, da kyautata kwarewarsu wajen gudanar da aikin.

Bisa kididdigar aka bayar, an ce, a cikin shekaru biyu da suka gabata, tawagar bada agajin jiyya ta kasar Sin ta sa hannu a cikin tiyata 2024, da sanya maganin kashe zafin ciwo ga majinyata 3151, da bada ceton gaggawa ga mutane 118, da yiwa mutane kusan dubu 10 allurar gargajiyar Sin. Banda wannan kuma, gwargwadon karfinta, tawagar bada jinya ta Sin ta bada aikin hidimar likitanci da horaswa ga mazauna wurin da Sinawa dake zaune a kasar, baya ga samar da jiyyar kyauta fiye da sau 10.

A watan Disamban bara, ministan kiwon lafiyar kasar Mozambique ya bada lambar yabo ga dukkan mambobin tawagar bisa kwazon da suka nuna.(Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China