in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamfanin Huawei na kasar Sin ya karrama abokan huldarsa mafi fice a Kenya
2019-03-29 09:43:44 cri

Kamfanin sadarwa na kasar Sin Huawei, da hadin gwiwar kamfanin bada hidimar sadarwar zamani na Redington Gulf dake kasar Kenya, ya karrama wasu abokan huldarsa wadanda suka fi yin fice guda 43 a kasar.

Taron karramawar da aka gudanar da yammacin ranar Laraba, ya ba kamfanin Huawei wani dandalin na nuna sababbin fasashohinsa na sadarwa, inda suma abokan huldarsa suka bayyana irin na su dabaru kan yadda za su bunkasa kasuwancinsu a Kenya.

An bada lambobin yabo 43 ne a fannoni daban daban da suka shafi tsarukan rage cunkoson sadarwa da sarrafa bayanai da horas da abokan hulda da kwararrun masu bada gudunmuwa a bangaren .

Shugaban kamfanin Huawei a Kenya, Stone He, ya ce aiki da kamfanin Redington Gulf da sauran abokan huldarsu na Kenya a bangaren fasahar sadarwa ya ba Huawei damar kai kayayyaki da hidimomin fasahar sadarwa kasar, wanda ya taimakawa musu gaggauta samun sauyin fasahohin zaman tare da biyan bukatun kasuwancinsu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China