in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Adadin mutanen da suka mutu a harin bom na Mogadishu ya karu zuwa 15
2019-03-29 09:40:48 cri
Wasu majiyoyi daga cibiyar kula da lafiya ta sanar da cewa adadin mutanen da suka mutu a sanadiyyar harin bam da aka sanya cikin wata mota a Mogadishu babban birnin kasar Somaliya ya kai 15 kana yawan wadanda suka samu raunuka yakai 17.

Abdulkadir Abdirahman, daraktan Aamin Ambulance, wato bangaren dake bada hidimar daukar marasa lafiya kyauta a Mogadishu, ta tabbatarwa kamfanin dillancin labaru na Xinhua cewa an samu karuwar mutanen da suka rasu a harin, sannan wadanda suka ji raunuka suna samun kulawar likitoci a asibiti.

Wata mota makare da ababen fashewa ta afka kan wani shahararren gidan sayar da abinci dake kan titin Makka Al-Mukarrama, lamarin da ya haifar da lalacewar gine ginen dake daura da wajen.

Shaidun gani da ido sunce harin bom din yayi muni matuka. "Ina kusa da wajen a daidai lokacin da motar dauke da bom ta kutsa ginin. Naga gawarwakin mutane a warwatse a yankin kuma tagogi sun tarwatse," Ise Awil, wani da ya ganewa idonsa ya tabbatarwa Xinhua.

Babu wanda ya dauki alhakin kai harin kawo yanzu, amma kungiyar 'yan ta'adda ta al-Shabab ta sha daukar alhakin makamancin harin a lokutan baya. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China