in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da suka rasu ya karu zuwa 11 sakamakon harin da aka kai a ma'aikatar 'yan kwadagon Somaliya
2019-03-24 16:49:48 cri
Wani jami'in kasar Somaliya a jiya Asabar ya ce, yawan mutanen da suka mutu ya karu zuwa 11, yayin da wasu 15 suka jikkata sakamakon harin da aka kai a babban ginin ma'aikatar 'yan kwadagon kasar a wannan rana.

A wannan rana da safe, aka tayar da bom da aka ajiye a cikin wata mota a gaban kofar ma'aikatar 'yan kwadagon dake Mogadishu, babban birnin kasar, daga baya dakaru masu dauke da makamai sun kutsa cikin babban ginin ma'aikatar, har suka yi musayar wuta da jami'an tsaron kasar ta Somaliya. Mataimakin ministan 'yan kwadagon kasar Saqar Ibrahim Abdalla ya rasa ransa sakamakon lamarin.

Daga bisani kungiyar Al-Qaida a Somaliya ta sanar da daukar alhakin kai harin. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China